1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu: Garanbawul a majalisar ministoci

Salissou Boukari
March 31, 2017

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya kori ministansa na kudi Pravin Gordhan, duk kuwa da adawar da abokan kawancensa suka nuna kan wannan batu, abun da ka iya kawo rarrabuwar kawuna a cikin jam'iyyarsa ta ANC.

https://p.dw.com/p/2aNnC
Südafrika I Präsident Jacob Zuma
Shugaban Afirka ta Kudu Jacob ZumaHoto: REUTERS/S. Hisham

Bayan da aka shafe tsawon kwanaki ana yada jite-jite kan wannan batu, sai da yammacin ranar Alhamis ce dai Shugaba Zuma ya aiwatar da sauye-sauye mai girma a majalisar ministocinsa. 

Ya nada sabbin ministoci 10 da mataimakansu 10. Wannan mataki ya haifar da faduwar canjin a kasar bisa fargabar abun da zai iya biyo bayan wannan sauyi.

Shugaba Zuma dai ya mika mukamin ministan kudin kasar ga wani na hannun damansa mai suna Malusi Gigaba, wanda a baya ya ke a matsayin ministan cikin gida.

An dai jima ana samun takun saka tsakanin Zuma da ministan na shi na kudi Gordhan, wanda a ranar Litinin da ta gabata shugaban ya nemi da ya dawo maza-maza daga wata ziyara da ya ke yi a Birtaniya.