Afirka ta Kudu: An kai hari a masallaci
May 10, 2018Talla
Lamarin da ya faru a arewa maso gabashin birnin Durban a garin Verulam, masu aiko da rahotanin sun ce mutane da suka aikata kisan kafin su shiga cikin masallacin sun bayyana kansu da cewar 'yan kasar Masar ne su. Har ya zuwa yanzu dai, ba a san dalilan kai harin ba, sai dai 'yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike.