1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Adadin wadanda suka rasu a sansanin Dikwa ya karu

Salissou BoukariFebruary 11, 2016

Mutane 58 ne suka rasu wasu kuma 78 suka samu raunuka sakamakon tagwayen hare-haren kunar bakin wake na sansanin 'yan gudun hijira da ke Dikwa a Jihar Borno.

https://p.dw.com/p/1HtaE
Nigeria Anschlag in Gombe
Hoto: picture-alliance/dpa

Babban jamiin hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya wato NEMA na shiyyar Arewa maso Gabashin Najeriya ya tabbatar da wannan adadi, inda ya ce a halin yanzu wadanda suka jikkata na can suna samun kulawa a asibitoci. 'Yar kunar bakin waken ta uku dai ta ki amincewa ta tayar da bam din da ke jikinta, bayan da ta yi la'akkarin cewa a kwai uwayanta da sauran danginta cikin wannan fili, inda daga bisani ta mika kan ta ga hukumomi.

Akwai dai sama da mutane dubu hamsin da ke zaman gudun hijira a wannan sansani kuma yawancin su sun fito ne daga kanan hukumomin Ngala da Kala Balge da Dikwa da Mafa da Marte da karamar hukumar Bama duk a jihar Borno. Wadan nan sabbin hare-hare na tayar wa mazauna yankin hankali a lokacin da suka fara sakin jiki tare da fatan da suke na komawa garuruwan su ba da dadewa ba.