A kalla mutane 8 ne suka rasa rayukansu a wani harin kunan bakin wake da aka kai a birnin Bagadaza.
February 1, 2006Talla
Rahotannin da ke iso mana daga birnin Bagadaza, sun ce a kalla mutane 8 ne suka sheka lahira, yayin da wani dan harin kunan bakin wake ya ta da bam a tsakiyar birnin Bagadaza da sanyin safiyar yau. Wata sanarwar da ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar ta bayar na nuna cewa, a kalla mutane 30 ne kuma suka ji rauni.
Harin ya wakana ne a unguwar Baab al-Sharjee, inda jama’a ke taruwa don neman aiki.
`Yan yakin gwagwarmayar Iraqin dai na iza wuta ne a yunkurin da suke yi na hambare gwamnatin kasar. Kawo yanzu dai, sun halaka dimbin yawan jami’an tsaro da kuma fararen hula a hare-haren da suke ta kaiwa a duk fadin kasar.