Ɓarin wuta a Mogadiscio tsakanin dakarun kotunan Islama da sojojin gwamnati
October 29, 2007Talla
A birnin Mogadiscio na ƙasar Somalia, a na ci gaba da ɓarin wuta, tsakanin mayaƙan sunƙuru, da dakarun gwamnati, masu sami goyan baya, daga ƙasar Ethiopia.
A tsukin kwanaki 2 da su ka wuce, ɓangarorin 2, sun yi faɗa mai muni, wanda ya sa dubunan mutane su ka ƙauracewa wannan birni.
A jiya lahadi, ɗaruruwan mazauna Mogadiscio, sun shirya zanga-zangar ƙin jinnin sojojin Ethiopia.
Sannan sojojin sun yi harbin kann mai uwa da wabi, wanda ya hadasa mutuwar mutane a ƙalla 3, tare da jima da dama raunuka.
A ɓangaren siyasa kuwa, a na ci gaba da taƙwan sako tsakanin shugaban ƙasa Abdullahi Yusf Ahmed, da paraminista Ali Mohamed Gedi.
A wani jawabi da ya gabatar jiya gaban yan majalisa, shugaban ƙasa ya buƙaci su tsige Praminista.