1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungyar al-Qaida a yankin Magreb ta yi iƙirarin kai harin Aljiyas

December 12, 2007
https://p.dw.com/p/CaUE

Babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki Moon ya yi tir da tagwayen hare haren bama bamai da aka kai jiya a Aljiyas babban birnin ƙasar Aljeriya yana mai cewa wani hari ne na matsorata. Daga cikin mutanen da suka rasa rayukansu a hare haren da aka kai da motoci akwai akalla jami´an MƊD 11. Ɗaya daga cikin bama-baman ya fashe ne a gaban wani gini dake kunshe da ofisoshin MƊD sannan daya bam din kuma ya tashi a kusa wata bas dake ɗauke da dalibai. Ma´aikatar cikin gidan Aljeriya ta ce mutane 26 suka rasu amma majiyoyin asibiti na cewa fiye da mutane 60 suka rigamu gidan gaskiya sakamakon fashewar bama-baman. Hukumomin Aljeriya sun ce mutane 177 suka samu raunuka. A cikin shafin ta na intanat ƙungiyar al-Qaida a yankin arewacin Afirka ta yi iƙirarin kai hare haren.