Ƙasashen Faransa da Jamus sun jadada aniyarsu na taimakawa Gerka
March 25, 2010Shugabanin ƙasashen Faransa da Jamus sun ce sun samar da hanyoyin taimakawa ƙasar Girka da ke fama da matsalar tatalin arziki,shugabannin wanda suka bayyana haka a birnin Brussel inda ake gudanar da taron ƙungiyar Eu sun ce za a yi amfanin da taimakon hukumar bada lamani ta duniya domin fitar da kasar Girka daga halin ƙaƙa nika yi. ƙasashe da dama na ƙungiyar tun da farko kamar su Faransa basu amince ba ba a nemi agaji mayan bankunan na duniya domin magance matsalar ta ƙasar ta Girka suna masu cewa wannan wani abu ne da ke iya nuna kasawar ƙungiyar ta EU wajen magance matsalolinta.Ana san ran a karshen taron da za a yi kwanaki biyu ana yi shugabanin ƙasashen na ƙungiyar ta EU zasu cimma dadaituwar baki da hukumomin na hukumar lamani ta duniya akan wani shirin taimakawa ƙasar girka da ƙuɗaɗen da zasu iya kai million 20 zuwa 30 na ƙudin Euro.
Mawallafi : Abourahamane Hassane Edita: Tijani Lawal